News:

Ramadan Mubarak!

I pray that we get the full blessings of Ramadan and may Allah (SWT) grant us more blessings in the year to come.
Amin Summa Amin.

Ramadan Kareem,

Main Menu

Wata sabuwa wai Gaddafi Yace A Raba Nijeriya Tsakanin Kabilunta

Started by bamalli, March 31, 2010, 12:47:12 PM

Previous topic - Next topic

0 Members and 1 Guest are viewing this topic.

bamalli

Gaddafi Yace A Raba Nijeriya Tsakanin Kabilunta 
Marubuci Ibrahim Alfa Ahmed
30/03/2010
 


Muammar Gadhafi

Shugaba Muammar Gaddafi na Libya ya bayar da shawarar a raba Nijeriya kasa-kasa tsakanin kabilunta kamar yadda aka yi ad tsohuwar kasar Yugoslaviya, domin kawo karshen tashin hankali a kasar da ta fi kowacce yawan jama'a a nahiyar Afirka.

Wannan furuci nasa na jiya litinin, ya biyo bayan shawarar da ya bayar a makon da ya shige cewa a raba Nijeriya tsakanin kasar Musulmi da ta Kirista domin a kawo karshen zub da jinin addini.

A bayan kalamin na sa na makon jiya, Nijeriya ta janye jakadanta daga kasar Libya, tana mai bayyana kalamun na Gaddafi a zaman "maras karbuwa", wanda kuma bai kamanci shugaban da ke kururuta hada kan Afirka ba.

A lokacin da yake mayar da martani a jiya litinin, Gaddafi ya sake nanata ra'ayinsa na a raba Nijeriya, amma a wannan karon ba kasa biyu ba, a raba ta zuwa kasashe da dama kwatankwacin kabilunta.

Ya kwatanta Nijeriya da tsohuwar Yugoslaviya, wadda ta kasu zuwa kasashe da dama a bayan rushewar tsohuwar Tarayyar Soviet.

Gaddafi ya ce duk wani matakin da za a dauka na raba kasar da dukiyarta, ya kamata a yi ta hanyar tattaunawa da cimma yarjejeniya ba wai ta hanyar zub da jini ba.


Bashir Ahmad

Gaskiya ni a tunani na Mu'ammar Gaddafi shugaban kasar libya maganarsa akwai kanshin gaskiya domin Nigeria tayi kabilu da yawa ga kuma rikice rikicen kabilanci.

Don't hate me, and don't hate Gaddafi.
Above All Fear Allah (S.W.A)