News:

Ramadan Mubarak!

I pray that we get the full blessings of Ramadan and may Allah (SWT) grant us more blessings in the year to come.
Amin Summa Amin.

Ramadan Kareem,

Main Menu

Jinkiri

Started by Mai sanyi, May 14, 2011, 11:48:54 PM

Previous topic - Next topic

0 Members and 2 Guests are viewing this topic.

Mai sanyi

Nai jinkiri akan soyayya harshe na yayi nauyi sosai
wadda zuciyata ke so kunya tai shamaki da abota

1. Ni a yau zare da abawa zan warware gare ku abokai
   zan batu akan soyayya ni lamarin ta ya dauren kai
   dan kwa naga babu ruwanta mai hada attajirai da musakai
   in taso tayo wani juyin sai ta hada talaka da musakai
   ni a yanzu tai min hadin da ban so ba ko ince na mugunta

2. Kunga kar kuce na zauce kaina kalau bara kuji sosai
   surkuki da sarkakiyar so na shige abin gwanin ban tausai
   wadda zuciyata ke so ta rurrufe ido da gilasai
   bata ma ganina amma sonta a zuciya yai rassai
   yanzu yaya zanyi in furta ko kuma azuci in fidda ta

3. Sanda ni na fara ganin ta saida tassakani narrike baki    dan kwa naga ta hadu sosai kyawun ta ne ya ban mamaki
   doguwa fara mai gashi hancinta mai tsaho har baki
   lokacin naso in furta sai naji ni nayi nauyin baki
   sai kawai na canja tunani ni da ita muka kulla abota

4. Yau da gobe hausawa sunce wai asara gun duk mai rai
   yanzu mun riga mun saba ni da ita ba batun bacin rai
   ban ganinta bata ganina saidai muna waya mai cinrai
   sonta ko yana dada yado zuciya kamar da an dasa tsirrai
   wannan makauniyar soyayya sai yaushe nikwa zan warketa?

5. So nake ku sani a hanya nai makuwa ina ta bulayi
   na rigada na shaida muku kome ake ciki ya zanyi
   sonta yazamo wani sashen raina taba shi jinya zanyi
   kunya ta hanani in furta ni jan'aji nake yin shayi
   kar naje na tafka asara na dade rabon da inga irinta

6. Tsuntsun so yana shawagi yaka yaka zo ka kai mini sako
   in ka tashi in kai gabas cikin garin da ba'a kyamar bako
   ka tambaya ina wadda sunana da nata yai kama daga farko
   zaka ganta mai kyawun sura sai ka zayyana mata sako
   kace ta ringa daukar haske domin ta gane duk mai sonta

      Alhamdulilla!
Da fatan sanaah yuseef (ummi) za ta karanta wannan waka danai domin ta
Umarmaisany

bakangizo

Ashe kai mawaki ne. Toh, Allah yasa Ummi taji