KanoOnline.com Forum

General => Culture => Topic started by: IBB on March 27, 2003, 10:28:08 AM

Title: Tatsuniya Online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on March 27, 2003, 10:28:08 AM
hey guyz how about tatsuniya online. eg Gizo da gogi. 'Yar

bora da 'yar mowa. ajebutters full here i dont know if una sabi

that one

gata nan kata nan ku, tazo mujita
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: sdanyaro on March 27, 2003, 04:47:26 PM
Assalamu alaikum;

This topic sounds very interesting. Can you please share with us one or more of the Tatsuniyoyin with us here? I think it is a good idea...
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Twinkle on March 27, 2003, 05:44:37 PM
UNCLE SALIS, BA'A YI MAKA TATSUNIYA BANE KANA YARO? KO DAYAKE DUK BATA BACI BA IBB BAMU MU SHA.. BARI NIMA NA ZAUNA NA TANKWASHE KAFA YADDA UNCLE SALIS YAYI A BAMU MU SHA!!!!!!!!!!! ;D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on March 29, 2003, 10:04:41 PM
IBB, ya ka fara abu kuma munji shiru??
To ni bari na bude mana filin ... ;)

Duk kun hallara? To madallah

Kunnen ku nawa...kara biyu ku sha labari... ;D

Gata nan Gata nan ku...

Gizo ne dai watarana yana tafiya, sai yaga wani katon sa! To shi wannan san girma ne dashi sosai wanda ko a shanun sarki babu mai girman shi. sai kuwa gizo ya tafi wajen Sarki yace mashi "sarki sarki kunnen ka nawa? sarki yace "biyu" gizo yace mashi "kara biyu kasha labari!!! yau naga wani katon sha!"

Gizo ya ja hanya suka tafi a ga wannan katon sa. Da aka je sai aka tarar wannan san na wata tsohuwa ne... akai mata dole aka ce sai an yanka shi!

Aka tambayi tsohuwa me take so a jikin san. Tace ita kayan ciki take so! Aka yanka sa, tsohuwa ta samu kayan ciki.

Tsohuwa ta kai kayan ciki gida ta ajiye har dai watarana suka zama 'yan mata masu kyawawa!

Sai watarana Gizo yana yawo sai yaga daya daga cikin 'yan matan!!! ay kuwa sai gaban sarki! yace "sarki sarki kunnen ka nawa? sarki yace "biyu" gizo yace "kara biyu kasha labari!!! yau naga wata yarinya kyakykyawa wadda ban taba ganin kyanta ba!!!

Aka ce to gizo ya ja hanya aje wajen da yaga yarinyar. Suka tafi da bafaden sarki zuwa gidan tsohuwa! Suka isa gidan aka ce ana Sallama da tsohuwa. Sai tsohuwa tace da daya daga cikin 'yan matan "ta hanji ta hanji debo ruwa ki kaiwa bakon da ke waje" ta hanji tace "uhm, na ci kwalliya, in debo ruwa in kai wa bakon da ke waje! sannu iya"

Tsohuwa ta cewa ta huhu ta kai wa bakon ruwa, itama tace abunda ta hanji ta fadi. Har dai sai da tsohuwa ta zo kan ta kitse, wadda kuma tafi duk 'yan matan kyau. Da aka ce ma ta ta kai ruwa waje, sai tace "to iya".

Ta kitse tana fita waje sai bafaden sarki ya dauke ta sai gudu! Ya kaiwa sarki ita, ya (sarki) aureta.

Sarki ya bada kashe di kar a sake a bar ta kitse tayi wani aiki na kusa da wuta. Su kuwa sauran matan gidan haushin ta suke ji! saboda tana da kyau sosai, gashi kuma sarki yana sonta! Rashin sa'a watarana sarki ya fita yaki, sai kuwa sauran matan gidan suka ce ay sai ta kitse ta fito tayi masu girki.

Saboda hakurin ta kitse, sai ta fito tsakar gida zata yi masu girki. ay kuwa da wuta ta buge ta! sai ta narke!!

Ashe wata tsunsuwa tana wajen ta gan me ya faru! Sai ta tafi wajen da sarki yake yaki tana waka tana cewa "sarki sarki a maida yaki baya ta kitse ta narke, ta narke ta zama ruwa sakar gida" tun sarki bai ji me tsunsunwa take cewa ba har dai yaji!

Sarki yana ji! sai kuwa ya hau dokinshi sai gida! yana zuwa aka zuba mata ruwa ta farfado ( ::)) ya tambaya waye yayi mata haka...aka ce mashi sauran matan ne. sai kwai sarki yasa aka gille masu kai!

Sarki da ta kitse kuma suka zauna cikin jin dadi....

kurunkus kan dan bera... da ban dan gizo ba da nayi karya...(lol)



Kai! in banda ta tsuniya ma, yaushe haka take faruwa... ::)

This sooo much reminds me of the olden days... ;D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Rose on March 30, 2003, 12:05:11 AM
Kai Ihsan! :D
Amma wallahi angaisheki
wannan irin tatsuniya kamar daga bakin granny :)
Agaskiya kintunamin da jiya
Think of some more please
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on March 30, 2003, 09:22:56 PM
l Ice...nima sai y atuna mun da baya :)

To gyara zama...ga wata nan tafe... 8)


Ruwan Bagaja

Gata nan gata nan ku...

Wani mutum ne yana da mata biyu;da mowa da bora. ko wace mace tana da 'ya guda daya. An sani bora da 'yar ta a gidan!

Watarana 'yar mowa tayi fitsarin kwance sai aka ce ay 'yar bora ce tayi dan haka dole taje kogin bagaja ta wanke abun da tayi fitsarin akai.

'Yar bora ta kama hanya ta tafi neman kogin bagaja! Akan hanyar sai ta hadu da wani kogi tace "kogi kogi ko kaine ruwan bagaja bagajar gayya ta dan sarki. domin kirgi aka aiko ni inzo in wanke a ruwan bagaja" And the kogi (river) replied "yarinya ni ba kogin ruwan bagaja bane. ni kogin tuwo da miyar taushe ne zauna ki ci idan kina so" 'yar Bora tace a'a ta gode amma ta koshi.

Ta kara yin gaba and she came across another river and asked it ko shine kogin bagaja and the river replied "yarinya ni kogin shinkafa ne da miya idan zaki ci zauna ki ci" tace aa ta gode amma ba ta ci.

She continued on her journey and came across another river...asked it same question and it replied "ni kogin alkaki ne da nakiya...da dai sauran irinsu". she said same thing to this river as she said to the other.

Tana ta tafiya tana wuce all sorts of rivers na kayan abinci har hadari ya hado...garin yayi duhu za'a yi ruwa! Then she saw a hut sai ta shiga ciki. Inside the hut she saw a thigh (YES A THIGH lol),a dog,a pot, rice, and some eggs

Tana shiga sai cinya tace "kan kan" sai kare yace wai cinya tana maki maraba.'Yar bora tace ta gode. Cinya ta kara cewa "kan kan" sai karen yace mata thigh din tace wai ta dauki kwayar shinkafa guda daya!!!ta girka masu.  She didn't argue. She cooked the single rice in the pot and it became da yawa har ya cika tukunyar.

Suka ci suka koshi. Next day tayi sai 'yar bora tace zata tafi neman kogin bagaja. Sai cinya tace "kan kan"  karen yace cinyar tace ta dauki eggs guda daya (big and small) taje wani waje dashi (can't remember the place) and say "in fasa" idan taji an ce "fasa fasa musha ruwan kawai" she shud not fasa it. But idan taji shiru sai ta fasa. 'yar Bora ta dauki karamin egg din tayi godiya ta ta kama hanya.

When she came to the place sai ta ce "in fasa" taji an ce fasa fasa musha ruwan kwai. Sai bata fasa ba tayi gaba. asked again but sai taji shiru, ta kara tambaya ta ji shiru...she asked three x b4 ta fasa.

Tana fasawa kuwa sai ga mutane akan doki...mutanen sun sha ado sosai ana ta busa algaita. Suka dora 'yar bora akan doki sai gida.

Suna shiga cikin gari sai garin ya fara kanshi yara suna ta binsu. Mutanen suka kai 'yar mowa har gida mamanta ta fito tana ta murna. Mutanen suka bawa bora da mamanta kudi sosai...sannan sai suka tafi. Bora da 'yarta suna ta murna.

Hmmm ashe anyi creating a monster!!! coz da mowa ta ga haka ya faru da 'yar bora, sai tace ay itama 'yarta sai taje kogin bagaja gobe...dan haka tayi fitsari gobe ta tafi wanke kirgi a bagaja.

The next day 'yar mowa set off in search of kogin bagaja. And she came across one river tace "kogi kogi ko kaine ruwan bagaja bagajar gayya ta dan sarki. domin kirgi aka aiko ni inzo in wanke a ruwan bagaja" And the kogi (river) replied "yarinya ni ba kogin ruwan bagaja bane. ni kogin tuwo da miyar taushe ne zauna ki ci idan kina so" and she replied "yau naji wani rin kogi!!! ina ganin tuwo da miyar taushen in wuce ban ci ba! lallai ma!!!" ta zauna ta ci tuwo ta koshi.

Ta kara yin gaba and she came across another river and asked it ko shine kogin bagaja and the river replied "yarinya ni kogin shinkafa ne da miya idan zaki ci zauna ki ci" nan ma tace lallai ma ya za'a yi ta wuce kogin shinkafa da miya...ta zauna ta ci ta koshi.

Tana ta tafiya tana wuce different kind of rivers na abinci and duk inda taje sai ta ci abinci. Dare ya fara yi ga kuma hadari ya taso za'a yi ruwa. Sai ta hango wata hut and sai ta shiga.

Da ta shiga sai taga cinya da kare (and all the things 'yar bora saw). Tana shiga sai cinya tace "kan kan" sai kare yace wai cinya tana maki maraba. 'yar mowa na jin haka sai kuwa cewa tayi "wannan wace irin cinya ce mai magan?? da kare mai magan?? yau naga ikon Allah" cinya ta kara cewa "kan kan" kare yace tace wai ki dauki kwayar shinkafa guda daya ki dafa. 'yar mowa tace ita kam ba zata dafa shinkafa daya ba! bayan ga shinkafar nan da yawa sannan wani ace ta dafa guda daya!!! ta debo shinkafa da yawa ta dafa! and the rice became kadan...basu ma koshi ba.

Next day tayi sai 'yar mowa ta shirya zata tafi sai cinya tace "kan kan" sai kare yace tace wai ki dauki kwai guda daya and go to some place and say in fasa...idan kinji an ce fasa fasa musha ruwan kwai, kar ki fasa sai inda kika ji shiru. 'Yar mowa tace tabdijan ina jin mutane sunyi magana inki fasawa?? lallai ma. 'yar mowa ta dauki big egg din and left without thanking the thigh and the dog!!

Tana zuwa wajen kuwa sai tace in fasa...sai taji ance fasa fasa musha ruwan kwai...ay kuwa sai ta fasa!!! hmmmm tana fasawa sai ga kuture da makafi on donkies gudaje sai binsu suke yi...ga wari da yake ta tashi!!!

Aka dora 'yar mowa kan jaki sai gida. Suna shiga cikin gari sai garin ya kama wari...yara sai gudu ake yi!!! Aka je kofar gidan su 'yar mowa mamanta ta fito ta tare ta...sai kuwa ta ga kutare da makafi...nan tai ta masifa wai 'yar ta ta kwaso mata gayyar wari da kazanta. Haka dai suka sauki mata 'yarta ba tare da sun bata komai ba sai rabon wari!!!

'Yar bora kuwa da mamanta suna can suna cin dadinsu...they lived happily ever after ~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~

Kurunkus kan dan bera...... till we meet again.... 8)
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on March 30, 2003, 09:25:50 PM
WHOA  :o amma fa na rubutu da kyau... da badan na gaji ba da na rubuta wata yanzu...but tomorrow insha ALlah... :)
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ibro2g on March 31, 2003, 02:31:48 AM
This is very interesting...I`ll make a rendevous here.
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on March 31, 2003, 05:46:21 AM
QuoteUNCLE SALIS, BA'A YI MAKA TATSUNIYA BANE KANA YARO? KO DAYAKE DUK BATA BACI BA IBB BAMU MU SHA.. BARI NIMA NA ZAUNA NA TANKWASHE KAFA YADDA UNCLE SALIS YAYI A BAMU MU SHA!!!!!!!!!!! ;D

kai dodon kodi. to zauna kasha tasuniya
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on March 31, 2003, 05:58:34 AM
gata nan ga tanan ku

wata rana sarkin abasha yasa gasar shan yaji. amma mutum

ba zai yi shan-jayi (shii) ba, wanda yaci gasar za'a bashi

sarautar rabin ragin inka fadi 'a kashe ka. kowa yace ba sai

iya ba. sai ga oga gizo yazo yace ai shi zaiyi aka ba shi jayi

yake sha dogari na tsaye akan sa. idan gizo ya sha ya sha sai

ya kalli dogari yace ai kaji ban ce shii ba ko in an jima sai ya

kara tambayar sa ko yace shii sai yace 'a'a.


TO BE CONTINUED
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Blaqueen on March 31, 2003, 10:27:15 AM
whao...
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: ummita on March 31, 2003, 11:57:40 AM
Quote
kai dodon kodi. to zauna kasha tasuniya

Wat amuses me d most iz wat IBB had, anywayz jjc'z cud b stupid @ tyms ::)...........du u know UNCLE SALIS sune masu nen wajen.......Did sum1 juss kall Salis dodon kodi :o :o(ummita fainted as well juss lyk her blad did) :-X
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on March 31, 2003, 07:54:13 PM
AM BACK and iiiiiitttttttttttt'sssss STORY TIME... ;D

Gata nan Gata nan Ku...

Daskindaridi

A wani gari da akwai wasu 'yan mata wanda suke living tare in one house. Da alkama, shinkafa, dawa, ... , and last but not the least, daddawa.

Sun sani daddawa kamar me. Komai ba'a yi da ita. Sai watarana aka yi shela a gari cewa duk 'yan matan gari su hadu a wani fili za'a yi gasa. Ita wannan gasar ta a yi guessing sunan dan sarki ne! duk wanda yayi guessing zai aure dan sarkin.

Su alkama, dawa, and the rest ana ta murna za'a tafi filin gasa. Ranar gasar ta zo duk 'yan matan suka ci kwaliyya banda daddawa saboda bata da abun sakawa! kuma sauran 'yan matan suna ta yi mata dariya.

Haka suka shirya suka tafi ba tare da daddawa ba. Abun tausayi daddawa ta saka 'yan kayanta wadanda take ji dasu ta kama hanyar filin gasa.

On their way, sai 'yan matan nan suka hadu da wata tsohuwa tana wanka a rafi. The old lady asked one of them to wash her back and the girl replied lallai ma iya baki ganin na ci kwaliyya ki ce wani na wanke maki baya! sannu ma. Duk a cikin 'yan matan nan aka rasa me wanke wa tsohuwa baya!

Bayan 'yan matan sun wuce sai ga daddawa ta taho. 'Yar tsohuwa tace mata dan Allah 'yan mata wanke mun bayana. Daddawa tace to iya... tana cikin wanke wa 'yar tsohuwa baya sai kuwa bayan tsohuwa ya burme  :o.

Daddawa ta rasa yadda zata yi! sai tace iya dan Allah yi hakuri bayanki ya burme. Tsohuwa tace me kika gani a ciki? tace wasu boxes guda biyu (big and small). Tsohuwa ta ce ta dauko small one din. When she opened (I can't remember what's inside the box) but I think kaya ne. Tsohuwa tace mata ta saka kayan.

Daddawa ta saka kaya tayi kyau sosai. The old lady then asked her ko ta san sunan dan sarkin? sai tace aa...and so tsohuwa whispered the name in her ear. Daddawa tayi godiya ta kama hanyar filin gasa.

A can kuma wajen gasar ana ta fafata da 'yan mata. Kowacce ta zo wajen dan sarkin sai ta gaya mashi sunan ta idan ya tambayeta sunan shi sai ta ce bata sani ba...shi kuma idan yaji haka sai yace koma da baya ki sha kuka...'yan mata sai kuka ake yi.

Ana cikin haka sai ga daddawa ta iso. 'Yan mata na ganinta sai aka fara zunden ta ana cewa ita kuma wannan daga ina? waya bata aron kaya? muma bamu san sunan shi ba bare ita? suna ta dai maganganu irin haka.

Ita dai daddawa bata ce komai ta karasa wajen tent din dan sarki
daddawa: "Assalaam salaam dan yaro, assalaam salaam"

dan sarki: "wacece nan take mana assalaam salaam"

daddawa: "daddawarka ce take maka assalaam salaam, me dadi a miya dan yaro, me dadi a miya"

dan sarki: naji naki suna yarinya kawo nawa suna

daddawa: daskindaridi dan yaro, daskindaridi

dan sarki: bude ki shigo yarinya, bude ki shigo ki sha dadi.
[/b]

Daddawa ta bude labulen tent ta shiga ciki...sauran 'yan matan suna ta jin haushi suna mamakin yaya aka yi ma ta san sunan dan sarkin!!!

The next day daddawa and daskindaridi got married and they lived happily ever after...

and this writer is tired and need some rest... ;D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on April 01, 2003, 06:11:48 PM
Me is Back... And today's story is...

Sarma Sarma du duf

Gata nan ga ta nan ku...

A wani a gari da akwai wata yarinya wacce tace ita baza ta aure kowa ba sai mara tabo (mark) a jikin shi!!! ko wani namiji ya zo wajen ta sai tace aa yana da tabo on his body.

Haka dai ko da yaushe take yi har watarana wasu doddani su biyu suka ji labari. Sai suka je gidan tururuwa suka yi wanka suka zama samari masu kyau.

Suka kama hanya sai garin da yarinyar take. Da suka isa sai suka karasa gidan su yarinyar. Aka yi masu sallama da ita ta fito. Da ta duba na farko ashe tururuwa ta chije shi a wuya dan haka sai tace ay shi yana da tabo. Sai second guy din he had nothing on his body sai tace to she'll marry him.

Suka yi aure and he took her to his house where he lives with his mother. First day bayan sun kwanta bacci ita da kanwarta (sister), sai kuwa suka ji a bakin kofa ana "sarma sarma du duf" ashe mother-in-law din ce
yarinya: wane ne nan yake mana sarma sarma du duf?

mother-in-law : uwar mijin ki ce taki miki sarma sarma du duf

yarinya: me kike so ki ke mana sarma sarma du duf?

mother-in-law: wuta nake so nake maki sarma sarma du duf

and then sai yarinyar ta debo wuta a kasko ta mika mata

yarinya: gashi nan ki diba ki bar mana sarma sarma du duf.

Da ta mikawa mother-in-law din, sai uwar mijin ta kase wutar and asked the girl for wuta again. They repeated the same thing as before and again uwar mijin ta kara kashe wutar. Suna tayin haka har gari ya waye sannan aka hakura. kuma duk hakan da ake yi lokacin maman miji ta zama dudanniya (not in her human form).

In the afternoon kuma sai kanwar (sister) ta tafi kai wa mijin yayarta abinci a gona (farm) sai kuwa ta gansu sun zama dodanni suna ta cin kwadi (frogs) :o. Ita kuma sai ta kama waka tana cewa "mijin yata ci da kwadi, mijin yata sha da kwadi"

Haka kullun wannan episode din yake faruwa between mother-in-law and her daughter -in-law and kuma kanwar matar and mijin matar.

Rannan dai suka (the girl and her sister) gaji sai suka hada plan na su gudu. Safiya nayi kuwa suka bi ta wani hole suka gudu. Da suka isa gida sai tace ita bata son auren.

Daga sannan bata kara duba tabo jikin namiji ba idan yazo wajen ta...har dai a karshe ta aure wani daga cikin masu zuwa wajenta...


:-/ :-/ :-/ hmmmm *scratching ma head*
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: ummita on April 02, 2003, 04:06:45 AM
U keep em cumin Ihsaneey we've got Gizo, Daskenderidi,Mora & Mora..............Nyc one babes ;)[/b]
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on April 02, 2003, 03:47:59 PM
;)keep it up Ihsan.

Ummi karki hada fada bada shi nake ba

here no be beef
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on April 02, 2003, 04:01:36 PM
cont from Gizo da shan yaji

BAYAN GIZO YA GAMA SHAN YAJI, SAI 'AKA KAISHI WAJEN

SARKI. KOKI MATAR GIZO TANA TA MURNA. SARKI YA

KALLI  :o GIZO YANA TAKAICI SABODA YACI GASAR KUMA

RABIN GARIN YA ZAMA NA SHI (GIZO). SAI SARKI YA

TAMBAYI DOGARI KO GIZO YAYI SHEII LOKACIN DA YAKE

SHAN YAJIN, DOGARI YACE 'A'A. SHI KENAN SARKI YABAWA

GIZO RABIN GARI. BASHI KE DA WUYA SAI GA KURCIYA TAZO

TACE AI GIZO YAYI SHEII LOKACIN SHAN YAJI. TA FADI

WAYON DA GIZO YAYI, YANA TAMBAYAR DOGARI KO YACE

SHEII. SHIKE NAN SARKI YA KARBE GARIN SHI YA KASHE

GIZO.  ???

KURUNKUS KAN DAN BERA
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on April 02, 2003, 04:04:57 PM
BA DAN KARYA, KARYA CE, IN FADA RIJIYAR ZUMA A CIRO NI DA GUGAR NAKIYA DA ALKAKI

IN TUNTUBE DA TUWON SHINKAFA IN DAUJE BAKI DA TSOKAR NAMA ;D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on April 02, 2003, 09:32:46 PM
Allah ya kara dawo dani filin tatsuniya...:) Tatsuniyar mu a yau ita ce...

GIZO YAYI AMARYA

Gata nan gata nan ku...

Gizo ne dai suna zaman lafiyar su shi da koki garin kalle kallen shi (irin na wasu...ban fadi suna ba!) ya gano 'yar gidan tururuwai (ants).

Gizo da debowa ya kai yace ay shi yana sonta zai kuma aureta!!!... su Gizo har da sakin koki!

Aka daura auren gizo and the ant aka sha biki aka gama aka kai amarya gidan gizo. Da farko kamar abun arziki ana zaman lafiya komai gizo yake so ana yi mashi.

After few month sai tsiya ta fara...tururuwa ta daina yiwa gizo abunda yake so! Ana haka sai rannan gizo ya hadu da koki a hanya

koki: ashe gizo an yame (rame), ashe gizo an yame?

Gizo: in bayi (bari) dai koki! nayi karambani da na auyo (auro) 'yar gidan tururuwai. Baki na ta maujeje (big), baki na ta kwalele (big), cikin ta kamar kwarya, kafar (leg) ta kamar tsinke (stick).

Koki tace ato that's ur own wahala... coz ita (koki) tayi kyau ( ::)) babu abunda ya dameta. Shi kuwa gizo wahala ta ramar dashi.

Nan dai gizo ya tsaya wai shi dai gaskiya koki ta dawo...he's tried of the ant! Koki sai da ta wahalar dashi sannan ta dawo! ita kuma 'yar tururuwa ya sake ta.

Gizo da koki suka koma kamar da tare da 'ya 'yansu. Gizo yayi kyau (ewww)...

Kurunkus kan dan bera da ba dan gizo ba dana yi karya...

Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: al_hamza on April 02, 2003, 10:32:11 PM
where do you come up with these stories from.
man this gizo na shan wahala a tatsuniyoyin hausa  ;D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on April 02, 2003, 10:41:46 PM
lol Ali...wallahi I all remember it from my childhood...:) insha Allah sai kuma gobe za'a kara saka wata...
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on April 03, 2003, 08:16:25 PM
:o NICE ONE IHSAN
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on April 03, 2003, 08:40:22 PM
KATA NAN KATAN KU

GIZO DA BASAMUDE


AKWAI WANI BASAMUDE A BIRNIN KUDUS. BASHI DA KOWA

SAI KATON SAN SA (HIS BULL) WANDA YAKE SAWA A GASAR

TABA KANSHI. SABODA YANA DA SAWO BABU WANDA ZAI IYA

TABA KANSA (HEAD) IDAN MUTUN  BAI TABA BA SAI YA CINYE

SHI. HAKA YAKE YI DUK SHEKARA WANNAN SHEKARAR SAI GA

SHI A GARIN SU GIZO YA NEMI WANDA ZAI TABA KANSHI YA

BASHI SA (BULL) DUK GARIN KOWA YAKI. GIZO NA JIN LABARI

SAI YAZO YACE AI SHI ZAIYI SHIKE NAN BASAMUDE YACE TO

AKA SA RANAR GASA, DA RANAR TAZO GIZO SAI YAKI

FITOWA DAGA DAKIN SHI, BASAMUDE YAZO BAKIN KOFA

YACE GIZO YA FITO GIZO YACE YANA ZUWA BASAMUDE YAI

TA JIRA DA YA GAJI YA KARA CEWA GIZO YA FITO SAI GIZO

YA CE YANA AIKI NE YA KUSA GAMAWA BASAMUDE YACE

WANI IRIN AIKI NE WANNAN SAI GIZO YACE AI YANA DINKE

BANGO BASAMUDE YACE DINKE BANGO? GIZO YACE E SAI

GIZO YACE MASA YA LEKO DAKIN YA GANI YADDA AKE DINKE

BANGO BASAMUDE CIKIN MAMAKI YA LEKA YANA ZURA

KANSHI CIKIN DAKI SAI GIZO YA TABA. GIZO YA FARA TSALLE

NA CABA (TABA) NA CABA JAMA'A SUKA SHEDA AI GIZO YA

TABA SHIKENAN GIZO YACI KATON SA

KURUNKUS KAN DAN BERE
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Rose on April 04, 2003, 12:08:13 AM
Another bunch Ihsan :)
Sannunki da aikin rubutu.

Kai su mallam gizo anzo duniya da kafar baya :D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on April 08, 2003, 05:39:05 PM
DARE DUBU DA DAYA
IF U WANT ME TO READ THIS BOOK 4 U HERE POST UR REPLY AS 'YES' NUMBER OF RESPONDS DETERMINE.............
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on April 16, 2003, 02:55:58 AM
Tatsuniya shiru kwana biyu  :) karatu yayi yawa shi yasa... but insha Allah idan na samu lokaci zan zagayo na rubuta ko daya ce....till then...take care all buh-buy
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: gogannaka on June 08, 2003, 05:06:10 PM
ga tanan ga tananku
gizo ne dai ya yiwo ciyawa ya kasa dauka sai ya dado wata ;D ;D ;D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: baby_gal_84 on June 08, 2003, 06:16:55 PM
wai sannu ihsan da kukari but plz tell us more ........gaskiya i miss childwood ayya my nanny i called her inna shes always the person tellin me tstsuniya and she died just a month ago ....ayya i miss her coz she never belive im old now shes alway pitin me like a baby tellin me stories and so on........ ihsan plz keep them comin me i cant remember all them in full ihsan do yu know the tstsuniya of i think yara ne da yawa daya tayi sata sai aka kaisu wajen wani kogi to find out or so i cant remeber all........plz if yu do tell us.
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: baby_gal_84 on June 08, 2003, 06:18:15 PM
wai sannu ihsan da kukari but plz tell us more ........gaskiya i miss childwood ayya my nanny i called her inna shes always the person tellin me tstsuniya and she died just a month ago ....ayya i miss her  :'( :'(coz she never belive im old now shes alway pitin me like a baby tellin me stories and so on........ ihsan plz keep them comin me i cant remember all them in full ihsan do yu know the tstsuniya of i think yara ne da yawa daya tayi sata sai aka kaisu wajen wani kogi to find out or so i cant remeber all........plz if yu do tell us.
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: MaAMaa_LagOS on June 10, 2003, 07:40:21 PM
Ga wani tsohon labari amma na manta da sunan sa..........


Gata nan gata nanku..............
Wata rana wani miciji ya shiga fada ya sari dan sarki bai sani ba ashe fadawa suna ganin shi. Suka bishi yayi ta gudu yayi ta gudu yana haki har ya kai wurin wani Bawan Allah ya gaya masa abin da ya faru. Bawa Allahnan sai ya tausaya masa ya ce "kasan mai zai faru?" ya ce "a'a". "Zan bude bakina ka shiga ciki na ka buya idan sun tafi sai ka fito". Maciji ya ce na gode ya shiga cikin bawan Allah. Fadawa su ka nemi maciji suka rasa. Bayan fadawa sun gaji sun koma fada, sai mutumin nan ya ce da maciji ya fito. Maciji yace ba zai fito ba wai shi ya samu wurin zama. Mutumin nan yayi yayi da macijinan ya fito ya ki.
   Ana nan anan mutumin nan ya rame sosai. Wata rana Allah ya hada shi da wani tsuntsu ya gaya ma tsuntsun abin da ya ke damun sa. Tsun tsun yayi dogon tunani ya ce ya san yadda za'a yi. Idan rana ta fito mutumin nan ya kwanta a rigingine a kan titi, idan macijin ya ji zafi zai fito shi kuma sai ya cin ye shi. Haka kuwa akayii maciji na leko kansa tsuntsun ya hadiye shi.                                                                
    Sai tsuntsun ya ci gaba da ba mutumin nan shawara ya ce "yadda ka rame haka ya kamata ka sami kaji biyu ka ba matar ka ta dafa ma ko ka ji karfi"
Mutumin nan sai yayi wuf ya kama tsuntsun nan ya ce "saura daya".
    Ya tafi da tsuntsun nan ya sa shi a keji ...........to be continued.
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: gogannaka on June 10, 2003, 10:29:01 PM
kai amma fa mutane da rashin kirki suke
pls maama dont tell us the guy went away with it
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: MaAMaa_LagOS on June 11, 2003, 06:36:58 PM
Mutumin nan ya kai tsuntsun gida ya sa shi a keji ya fita ya sayo kaza ;D a hada da tsuntsun ka ga an sami biyu kenan.
    Matar mutumin nan ta ga tsuntsun a keji yana ta kyarma. Sai ta tambaye shi mai ya hada shi da mallam har ya kamo shi ya sa a keji? Sai tsuntsun ya kwashe labarin yadda sukayi da mutumin duk ya gaya mata. Ita kuwa tausayin shi ya kamata ta bude keji ta ce "Fita ka tafi Allah ya saka ma". Fitowar tsuntsu ke da wuya sai ya yo kan baiwar Allahnan ya kwakwale mata ido daya ya tafi abinshi. :'(
   kurunkus kan dan bera.
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: baby_gal_84 on June 14, 2003, 12:09:42 AM
tau ina ruwan kuwa da nasa hali kenan.... a takaice dai matar mutumen ce kadar mai kirki .... amma ita ma wa ya sani maybe tana da nata mugun hali....
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on June 14, 2003, 07:22:34 AM
maama lagos this story has to have part three. the snake reloaded  ;D ;D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Guduma on August 06, 2003, 02:13:30 PM
Gata nan gata nan ku.

Anyi wani mutum a wani kauye wanda ke da sana'ar fatauci da jakunansa biyu. A kullum sati ya kan tafi da jakunansa cin kasuwoyi inda yake yin kwana biyu, ko uku watarana. To, shi wannan mutum Allah ya bashi kyakykyawar mace, wacce  kauyensu kaf, babu mace mai kyanta. Ita wannan mata kuwa fasikace ta kin kari, domin a kullum mijinta yayi tafiya, to fasikan garin maza sai suyi layi a kofar gidansa, wani ya shiga ya fito, wani kuma haka
Rannan wani yana cikin dakin matarsa ya dade sosai bai fito ba, har wanda ke jiransa ya gaji, abin ya dami shi wanda ke jiran har ya rasa abin da zai yi. Can yana zaune, ya kuntume don fushi wanda ke cikin dakin, sai dabara ta fado masa. Ya nemo tsumagiya mai kyau ya zo da ita kofar dakin ya dinga dukan kasa yana wani karaji da gunji kamar dai na jakuna dake tafe, wato domin matan nan da wanda suke tare su ji, su zaci cewa kila maigidanta ne ya dawo.
Mutuminnan dai ya ci gaba da kartar kasa har matan ta ji, sai tace wa kwartonnan, "wai! ai ga mijina ya dawo! yaya zanyi da kai, ni 'ya su?". Sai kwarton yace "ki bude mini kofa da sauri, sai na fita a guje, ta yadda ba zai ganni ba balle ya ganeni". Ta ce "to". A kofar daki kuwa wancan kwarto yana jinsu, sai ya make da tsumagiyarsa a hannu, yana jira na cikin dakin ya fito. Can sai ya ga an bude kofa da gaggawa, sai ya ga wanda ke ciki ya fito a guje, ya nufi kofar gida. Sai shima yayi wuf, ya bishi ya dinga tsala masa bulala har ya kaishi bayan gari. Wanda ake duka yana jin zafin duka, amma ba daman yayi ihu don gudun tonan asirinsa, sai kawai dai yana ta gudu, wannan ko sai shirga masa bulala yakeyi har ya kaishi nesa tukun ya dawo gun matannan.
To kasan kauye, baa rasa matattara inda mutanen gari ke haduwa ana hirar yau da kullum. To suma kwartayennan biyu washe gari sai suka fito gindin wata itaciya tareda sauran jamaa suka zauna. Sai kwarton da aka yiwa bulala sosai jiya da dare yace, " ashe malam mai jakai ya dawo?" Shi kuwa wanda ya tsuga masa duka ya ce, "aa, ai malam maijakai bai dawo ba, kila sai jibi". Da wanda aka dokannan yaji haka, sai yayi shiru yana mamaki cewa an cuceshi jiya da aka fasa masa jiki da bulala, yana tsammani mijin matar ne. Sai ya ce  " ;Din kuwa mai jaki bai dawo ba, to lalle kauyennan namu akwai azzalumai!!".
Kurungus kan bera, wanda yaji tsoro.................
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: kilishi on August 06, 2003, 03:57:03 PM
A story of a jealous man and what befell him
This is a story about a jealous man.

A story, a Story. Let it go. Let it come.

There was a certain man who used to live in a town, but afterwards he rose up and went to the bush, lest people might go after his wives, until one day the chief of the town heard about him and he said, 'He who goes and seduces his wives, if he comes (to me) I will give him a horse, and a cloak, and one hundred thousand cowries.'

Then a certain man said he would be the one to go and lie with his wife before his eyes. Then he went off and sought some baobab seeds. He opened them, (and) cleaned out the inside well; he sought for some very small pieces of money and poured them inside. He went, reached (the place where the man was) (and) gave him a present of them.

When he broke (one) open he saw the small money inside. He broke another also, (and) in the same way broke open another. And he said, I My friend, will you not show me where this baobab tree is?' He replied, The place where this baobab tree is is far away.' (And) he said, Take me (to it).' And he said, 'It cannot be climbed except by a ladder, (and) no one knows where it is save me.'

And he continued to entreat him; and at last the seducer said, I Let us go, I will take you there, but if it was not for you, I would not show any one the place.' So they set out along with his wife. When they came to the baobab tree then the seducer lifted the ladder and placed it (against the tree), (and) told the woman's husband to climb up. So up he climbed.

When he had finished climbing, then he lifted away the ladder, (and) carried it somewhere else (and) set it down, (and) came back. He seized the wife and threw her down. He did what he intended, the woman's husband looking on (and) not able to descend; but he said, 'I shall spit on you, I shall spit on you,' until they had finished what they were doing.

The seducer went his way. He came, (and) told the chief what they had done. The chief gave him his reward, and added to his gifts. He said, 'That's the medicine he required.' As for the (jealous) man, his wife with difficulty lifted the ladder, (and) brought it to him, (and) he descended. On his return home he collected all his goods, (and) returned (to live) in the town. He said, 'My jealousy dragged me into this; if I remain here, people will destroy me.'

That is the story.

Off with the rat's head.
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on September 17, 2003, 08:41:38 PM
a wani gari anyi wata mata wacca duk lokacin da mijin ta yai tafiya sai kwartaye su fara hallara 'a gidan.
wata rana mijin yayi tafia sai kwarto yazo, kwarton nan na cikin daki sai mai gida ya akayi ya akayi bai samu tafiya ba sai ya dawo, mai gida yazo yana buga kofa yana sallama sai matar tace wa kwarton muryar mai gidan ta take ji, suka fara tunanin yadda za suyi sai matar ta tuna tana da katuwar-tukunya (big pot) a karkashin (under) gado shiken kwarto sai ya shiga ciki ya buya. mata ta fito ta bude wa mai-gida gida ya shigo suna daki 'a zaune da kuma kwarto 'a tukunya, sai ga wani kwarton yazo kuma yana kwankwasa (knocking) kofa sai matar tai sauri tace wa mijin ai masu karbar tukunya ne suka zo. shike nan sai mai gida ya dauki tukunya ya bawa mai knockin da mai-knockin yai gaba sai yace kai allah yai mani gyadar dogo sai wanda yake cikin tukunya yace allah ya maka gyadar dogo ko allah yai min
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: kilishi on October 14, 2003, 03:05:03 PM
I B B ashe ka iya tatsuniya haka? lallai matar shu'umar gaske ce,wato dai ita ce da luck!!! Allah kyauta. ;D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Anonymous on October 15, 2003, 03:30:43 PM
badan karya karya ce in fada rijiyar zuma a ciro ni da gugar nakiya da alkaki in tuntube da tuwon shinkafa in dauje baki da tsokar nama :o
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: gogannaka on October 19, 2003, 03:12:05 AM
Quotebadan karya karya ce in fada rijiyar zuma a ciro ni da gugar nakiya da alkaki in tuntube da tuwon shinkafa in dauje baki da tsokar nama :o


Wayyo dadi!!!!!!!!!
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: zezezee on October 30, 2003, 09:16:54 AM
hmmmmmmmmmmmmmmm...su ihsan manya!
hajjaju akwai ki fa ;D
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on January 12, 2004, 05:09:52 AM
Gatan gatan ku.

A wani gari mai suna Shangai a cikin kasas Sin anyi wani jarimin Sarki mai dukiya. Allah bai bashi haihuwa ba. bayyan anyi ta rokon allah da kuma tsubbace-tsubbace sai yar autar matar sa Allah ya bata ciki, da sarki yaji labarin matarshi tayi ciki sai sonta ya shiga zuciyar sa sosai. sarki yasa akai ta kula da matar nan da kyau har ta sauka, ta haifi da na miji, sarki ya sami magaji.
dan sarki ya kawo karfi aka koya masa sukuwa da doki da duk abun daya kamata ya iya.

Mean While

a wani nan kauye mai suna Bankok akwai wata yarinya mai kyan-hali, iyayenta sun mutu tun tana yar-karama, uncle dinta ya dauke ta take mashi aiki a gidan sa. sai yan-gida they took advantage of that suke gana wa yarinyar nan azaba ta tashin hankali, itace debo ruwa, girki, wanki, shara, abu kadan duka.

Sarkin Sin dansa ya isa aure, sai yasa akayi shela; duk 'yan-matan garin dana kauye suyi kwalliya su zo, Yarima zai zabi matar sa, amma da sharadi. sharadin kuwa shine sai ta fadi sunan sa (shi dan sarkin).

mata aka shiga kwalliya. ranar aure tazo. 'Yan-mata kowa ta cancara kwalliya sun dau hanya zuwa fada. amma yar baiwar Allah babu kayan kalliya.

'Yan-matan nan na tafiya sai ga wata tsohuwa tazo, tace 'dan allah 'yan-mata wacece zata iya wanke min baya na hannu na ya tsufa bazan iya ba'. 'yan mata suka kalle ta 'a wulakance sukace munyi kwalliya zamu ga yarima san nan za mu tsaya miyi miki wanka Allah ya sauwake.

kowace yarinya idan tazo sai tsohuwar nan ta tare ta ko za tayi mata wanka amma su ki. sai ga wanna yarinyar da iyayenta suka mutu ta zo tsohuwa ta roke ta, ta wanke mata baya yarinya tace to baba. tana cikin wanke mata baya sai bayan ya rufta (broke) tsohuwa ashe ba mutum baceba, sai tace mata ya haka kowa zai tafi fada yayi kwalliya banda ke yarinya tace bani da kaya. sai tsohuwa tace 'ki dauki wannan dan-basket din dake cikin bayana ki bude'. da yarinya ta bude sai ga kaya masu dan-karen-kyau suna kamshi taba bawa yarinya, yarinya ta karba tace na gode ta kama hanya sai tsohuwa ta tsayar da ita.


srry got 2 rush do sumtin will be updated as soon as pos
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on January 18, 2004, 12:54:15 PM
Quotehmmmmmmmmmmmmmmm...su ihsan manya!
hajjaju akwai ki fa ;D
??? zezezee, me no get u woo

anywayzzz...now that I am back, insha Allah more tatsuniyas to come.
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: kilishi on February 12, 2004, 07:44:21 PM
All right.  A tale for you.  There was a man, a famous malam and an emir s son.  He had his daughter; the other was an only son.  He said, he said ... he went to see the old woman to whom the em... the malam had entrusted his child.  He said to her, Hey, can you do that ... call the malam s daughter so we can talk to her?
She replied, Yes, I ll just go tell her. So they went off. When she got there she said, The emir s son says he d like to talk to you.
She answered, When you go back, tell him I ll set a mortar on the wall and we can talk.
That was that.  She went back and told him.
That was that.  They went to the wall at night and chatted.  Everyday that s what they did.  Everyday that s what they did.  They d talk by the wall.
That s how it was until one day he said ... he got up and said that he wanted to marry her.
That was that.  But the malam replied, Me, I refuse to give her up.   He continued, I m going to marry my daughter to a koranic student.
He said, No.
She insisted, Father, let me marry him.  I want to marry him.
 He said, All right.   That s what they did, and it was finished.  That s how it was.  The marriage was performed.
When it was finished ... when it was finished, time passed and then one day--but he already had one wife.  He took some stones and gave them to the malam s daughter.  And he took some rice and gave it to the other wife.  He told them to boil water.
She went to her parents home and complained, Oh Father, he gave me stones and told me to boil, no ... to boil stones.  And he gave her rice and told her to cook it. He replied, Go and find a single grain of rice.  Find a single grain of rice, put it in those stones, and heat some oil.
That was that.  She went and got her grain of rice and put in some oil.  That was that.  Hers all became rice and the other woman s became stones.
He came and said, Bring me what I gave you to cook. First he went to the head wife and saw that hers had all become stones. That was that.  Then when he went over to the malam s child he found rice.  That was that.
That was that.  Time passed, and he felt something wasn t quite right.  So he took his horse ... he told her ... he took a mare and said to her, You see this mare?  Before I come back she s to have a colt that looks like my horse.  As for me, before I return, you, you re to have a son that looks like me.
That was that.  She went crying to her father and said, Father, as he was getting ready to go off to another country he told me that before he gets back the mare is to have a son that looks like his horse, and I m to have a son that looks like him.  But I m not pregnant and his mare isn t pregnant
He replied, Go off and wait. He performed some work for her and said, Wherever he stays, wherever he sleeps, you ll sleep there.  Wherever he spends the afternoon, that s where you ll spend the afternoon.
She mounted her mare and off they went.  Where he spent the afternoon, she spent the afternoon; where he slept, she slept.  When he stopped, where he stopped, that was that, she too stopped there.  Drummers were sent out to announce that there was a newly arrived divorc?e for anyone who wanted her.  When he heard he got up and went, and when he arrived he demanded, Young lady, do you want me?
She replied, It s been a long time I ve wanted you. He said, But if you want me, she said, you ll have to mate your horse with my mare.
That was that.  He answered, It s as good as done. When morning dawned, his mare and her horse were mated.
As for her, he came to her rooms.  She said, You see, I don t want anything from you except your ring, your perfume jar, and your blanket.
He responded, It s done.   That was that.  He gave them to her.  Once he d given them to her, she got back on the road and headed home.  On and on and on she went.  By the time he returned she d come back pregnant with his child and the mare was pregnant with his horse s child.  That s how she returned.
By the time he got back she d had the child.  As he made his greetings someone said, Here s your husband come back.   That was that.  When she was told, Here s your husband come back, then she picked up the child and held him in her arms in front of him.  Then she brought out the ring and put it on; she brought out the blanket and placed it over his shoulders; she brought out the perfume jar and set it in front of him.  When he got down from his trip he didn t go anywhere until he d gone to see the mare.  When he arrived, he saw it was his horse s son.  And then as he drew close to the house he saw her sitting with the child.  He looked exactly like him and he had on all his things.  He asked her, Hey, where did you get these things?
She replied, Where did I get these things? She went on, You see, you see them here, period.
That was that.  He said to her, Yes indeed, your father has become a very famous man.  Let s live together as a married couple.
She replied, Me, I m not staying married to you. She said, If you want the two of us to stay married, I swear, you ll have to get rid of your other wife.  Me, we can live here together. That was that.  He got rid of the other wife, and stayed with her.
K ungurus!  Off with the mouse s head
Title: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on December 03, 2004, 06:06:40 PM
oh...haven't seen this tatsuniya before. Quite..err...interesting :)

Well it has almost been year since anything was posted here! I actually can't think of of any tatsuniya right now...even if i do maybe i have already posted it. But let me try...here we go...

Gata nan gata nan ku...

Da akwai wani mutum dake da mata biyu dukkansu kuma suna da 'ya ya. To sai watarana uwargidan ta mutu a bar danta mai suna Janiya. Amaryar dama bata san uwargudan da danta! Ay kuwa shikenan ta samu abunyi; tayi ta gallazawa yaron, ba abinci sai aiki. Yaranta kuwa kuda ma baya taba su. To shi wannan yaron ya gaji wata saniya daga wajen maman shi. Ita dai saniyar nan tana magana dan haka duk wani tuggu da amarya ke shiryawa Janiya, saniya tana gaya mashi. Amarya taga tayi duk wani abu gashi har Janiya bai mutu ba. Sai rannan Janiya ya je wajen saniyar shi sai saniyar ke ce mashi "amarya zata sa a yanka ni, ka ce kana son kayan ciki". Haka aka yi kuwa, amarya ta sa aka yanka saniya, Janiya ya karbi kayan ciki.

To yau ma dai uwargida ta hada wani tuggun...da Janiya yaje wajen kayan cikin saniya sai ta ke ce mashi " Janiya Jannati, kishirya uwa ba uwa ba ce, Janiya Jannati...yau zata saka wuta a daki...kada ka kwata a gaban gado."

Dare yayi aka zo kwanciya...to dama kan gadon da dan amarya da Janiya ne. Janiya ya tafi can bayan gado ya kwanta. Ay kuwa bacci yayi bacci dan amarya ya murgino sai cikin wuta. Ya fara ihu yana cewa "iya nine, iya ni ne!" Ita kuwa tana can kwance da jaririnta tana cewa dama kai ne mana dan ubanka!

Washegari amarya ta tashi wai taga Janiya ya mutu...amma ina sai gawar danta ga Janiya kuma da ranshi! Karshe dai amarya haukacewa tayi!

Kurunkus kan tan bera...da badan gizo ba da nayi karaya...dama dai ....hehe
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: mlbash on December 21, 2004, 10:17:14 PM
Quote from: "UmmAyman"Tatsuniya shiru kwana biyu  :) karatu yayi yawa shi yasa... but insha Allah idan na samu lokaci zan zagayo na rubuta ko daya ce....till then...take care all buh-buy

MUNANAN MUNA JIRA, ALLAH YABADA SA'A KUMA.
Title: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Anonymous on May 06, 2005, 07:28:25 AM
gogannaka I completely agree with yor argument.
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on May 24, 2007, 02:11:36 AM
c'mon people lets revive this room anybody got more tatsuniya to share with us. lets save them for the younger ones
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: jaybee on May 24, 2007, 12:34:09 PM
Assalam Alaikum Ihsan,
A gaskiya na ji dadin Tatsuniyarki ta Diskindaridi, sai dai kash kina amfani da abin nan da ake kira Ingausa wajen bayar da labarinki. Don Allah ki daure ki daina hada Ingilishi da Hausa, idan Hausa, Hausa kawai, idan Ingilishi, Ingilish kawai. Da fatan ban bata miki rai ba. A huta lafiya.
Jibril
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on May 31, 2007, 10:46:17 PM
Quote from: jaybee on May 24, 2007, 12:34:09 PM
Assalam Alaikum Ihsan,
A gaskiya na ji dadin Tatsuniyarki ta Diskindaridi, sai dai kash kina amfani da abin nan da ake kira Ingausa wajen bayar da labarinki. Don Allah ki daure ki daina hada Ingilishi da Hausa, idan Hausa, Hausa kawai, idan Ingilishi, Ingilish kawai. Da fatan ban bata miki rai ba. A huta lafiya.
Jibril
Ale JB thanx 4 the advise we will take that into consideration
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Fateez on June 01, 2007, 10:55:48 AM

Nice tatsuniyoyi here. I never really got to read them until now.

Daskin da ridi was my favorite those days. Dunno if i'm the best

person to tell tatsiniyoyi but i can suggest a few i remember.


Anyone heard of these??  
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on June 03, 2007, 05:03:24 PM
Ah Fateez you really bring back memories for me i know all these tatsuniyoyin but cant remember how they go. Haj Fateez can u do us a favour and share with us if u can remember. Members we will be waiting for your contribitions
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Fateez on June 03, 2007, 08:14:28 PM


Hehe, Anya kuwa? Nima fa I remember them mostly by the songs and then a

bit of the story but not 100% kuma I'm not really a good story teller........ 8)

Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: Ihsan on June 08, 2007, 11:05:51 PM
Quote from: jaybee on May 24, 2007, 12:34:09 PM
Assalam Alaikum Ihsan,
A gaskiya na ji dadin Tatsuniyarki ta Diskindaridi, sai dai kash kina amfani da abin nan da ake kira Ingausa wajen bayar da labarinki. Don Allah ki daure ki daina hada Ingilishi da Hausa, idan Hausa, Hausa kawai, idan Ingilishi, Ingilish kawai. Da fatan ban bata miki rai ba. A huta lafiya.
Jibril

Nagode jaybee. Wani lokacin ne sai an dan garaya.
Fateez, I think na bada tatsuniyar Janniya.  I know ruwan bagaja and Nagoma (though can't remember what happened at the end of nagoma). I knind of remember the barewa girls but can't put it in place. I'll try and post ruwan bagaja when I get the time insha Allah.
Title: Re: tatsuniya online (GIZO DA GOGI)
Post by: IBB on June 10, 2007, 11:56:15 AM
Nice 1 Ihsan keep them comin
Title: Re: Tatsuniya Online (GIZO DA GOGI)
Post by: bakangizo on September 16, 2011, 12:26:06 PM
Aaah!! How could we allow this forum to die like this? :'( Going through this thread makes you realize how rich, entertaining, educating and interesting the forum was. I've seen facebook and twitter, and honestly I love this place more personally.